Posts

Showing posts with the label Siyasa

KALLI ALJANIN DA AKE TUNAIN YA HALARCI TARON KWANKWASIYYA

Image
KALLI ALJANIN DA AKE TUNAIN YA HALARCI TARON KWANKWASIYYA Wata halitta da jama'a suke tunanin Aljani ne ya bayyana cikin suffar dattijo 'WAI' ya sauko daga sararin samaniya a kan keke, lokacin da ake taron Kwankwasiyya a karamar hukumar Birni. Da mutane suka tambaye shi, me ya kawo ka? Sai yace "Nazo ne domin naga Kwankwaso" Sarauniya.

Kannywood Atiku zata zaba>>Yakubu Muhammad

Image
Kannywood Atiku zata zaba>>Yakubu Muhammad Taurarron fina-finan Hausa, Yakubu Muhammad ya bayyana cewa, masana'antar Kannywood dan takarar shugaba kasa na jam'iyyar PDP, Atiku Abubakar zata zaba saboda suna fatan zai tallafa musu idan ya zama shugaban kasa. Yakubu Muhammad ya bayyana hakane a wajan wani taro na musamman da wakilan Atiku Abubakar suka yi na jin ra'ayin jama'a a Kaduna, kamar yanda Punch ta ruwaito. Yakubu yace suna yin fina-finai marasa inganci wanda matsalar rashin shugabanci na gari ne ya jawo hakan. Sannan a lokacin mulkin tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan zai iya tuna cewa, ya bayar da tallafin miliyan 200 ga masana'antun nishadantarwa. Dan haka Atiku zasu yi.

Idan dai kunji dadin mulkin Buhari to ku sake zabenshi>>Atiku

Image
Idan dai kunji dadin mulkin Buhari to ku sake zabenshi>>Atiku Dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar PDP, Atiku Abubakar ya bukaci 'yan Najeriya dasu sake zaben shugaban kasa, Muhammadu Buhari a zabe me zuwa muddin dai sun ji dadin mulkin na Buhari. Atikun ya bayyana hakane a wata sanarwa da ya fitar ta hannun me magana da yawunshi, Phrank Shuaibu inda yace, a duk fadin Duniya babu inda ake samun shugaban kasa da bai tabuka abin arziki ga 'yan kasa ba amma kuma ya fito yana so a sake zabarshi. Yace shugaba Buhari kara saka Najeriya yayi cikin matsala a mulkinshi kuma kasashen Duniya dama 'yan Najeriya sun yi ittifakin cewa bazai ci zaben da za'a yi ba saboda 'yan Najeriya sama da miliyan dari basa iya cin abinci koda sau daya a rana dan haka suna cikin yunwa kuma suna fushi dashi, ba zasu saka mishi kuri'a ba. Vanguard ta ruwaito cewa, Atikun ya kara da cewa,  ga duk wanda yasan ya samu aikin yi a karkashin gwamnatin Buhari to ya zabi Buharin wanda kuw...

Ban yi Allah wadai da dakatar da alkalin alkalai ba>>A'isha Buhari

Image
Ban yi Allah wadai da dakatar da alkalin alkalai ba>>A'isha Buhari Uwargidan shugaban kasa, Hajiya A'isha Buhari ta karyata wasu labarai dake watsuwa a shafukan sada zumunta cewa wai ta yi Allah wadai da dakatarwar da mijinta, shugaban kasa, Muhammadu Buhari yawa alkalin alkalai na kasa. Hajiya A'isha ta hannun me magana da yawunta, Sulaiman Haruna ta bayyana cewa ba ta yi magana akan dakatar da alkalin alkalan ba kuma ta yi kira ga masu watsa cewa ta yi maganar da su daina daga yanzu.

Ya Allah ka zaba mana wanda yafi zama Alheri tsakanin Buhari da Atiku>>Kumurci

Image
Ya Allah ka zaba mana wanda yafi zama Alheri tsakanin Buhari da Atiku>>Kumurci Tauararon fina-finan Hausa, Shu'aibu Lawal, Kumurci, wanda yana daya daga cikin taurarin fina-finan Hausa wanda ke bayan Atiku, yayi wata addu'a da ta dauki hankulan mutane, inda yace idan Buhari ne Alheri, Allah ya bashi idan kuma Atiku ne Alheri Allah ya canja mana ya bashi. Gadai abinda ya rubuta kamar haka: BISMILLAHI ALLAH kazaba mana shugaba nagari mubamusan komaiba, Allah sai abinda kasanar damu, idan baba buhari Alkairine Allah kabashi idan kuma ba Alkairi bane to Allah ka gaggauta canjashi kabawa baba Atiku idan shidin alkarine ga wannan kasa tamu Allah ka amsa dan karfin mulkinka da son Annabi (S A W) SUBHANAKA LA ILMU LANA ILLA MA ALLAMTANA INNAKA ANTAL ALIMUN HAKIM

Biyora ya samu kyautar mota bayan da ya mayar da Atiku wadda ya bashi

Image
Biyora ya samu kyautar mota bayan da ya mayar da Atiku wadda ya bashi Sanannen me kare muradun shugaban kasa,Muhammadu Buhari a shafukan sada zumunta wanda ya koma goyon bayan Atiku na dan wani lokaci, har aka bashi kyautar mota, sannan daga baya ya dawo bayan Buhari ya kuma mayarwa da Atiku motar da aka bashi, ya koma hawan babur dinshi da ya saba, yanzu dai an bashi kyautar wannan motar Da ake ganin hotonta a sama. Biyoran ya bayyana a shafinshi cewa an shirya mai wata walima ta musamman ta dawowa jam'iyyar APCn da yayi sannan aka bashi kyautar wannan motar.

Ina goyon bayan shugaba Buhari dari bisa dari kan dakatar da Alkalin alakalai

Image
Ina goyon bayan shugaba Buhari dari bisa dari kan dakatar da Alkalin alakalai Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya bayyana goyon bayanshi dari bosa dari ga shugaban kasa, Muhammadu Buhari kan dakatar da alkalin alkalai, Walter Onnoghen da yayi.

Hotuna daga walimar da shugaba Buhari ya shiryawa jiga-jigan APC

Image
Hotuna daga walimar da shugaba Buhari ya shiryawa jiga-jigan APC Shugaban kasa, Muhammadu Buhari kenan a wadannan hotunan yayin da ya hadawa jiga-jigan jam'iyyar APC walima ta musamman a fadarshi ta Villa dake babban birnin tarayya, Abuja. Akwai gwamnoni masu ci da 'yan takarar gwamnan na jihohi daban-daban da sauran wasu kusoshi a jam'iyyar da suka halarci taron.

Tsarin Trade Moni salon sayen kuri'ane da wayau>>Transparency International

Image
Tsarin Trade Moni salon sayen kuri'ane da wayau>>Transparency International Kungiyar kula da rashawa da cin hanci ta Transparency International ta bayyana cewa tsarinnan na Trade Moni da gwamnatin shugaban kasa, Muhammadu Buhari ke bayarwa ga kananan 'yan kasuwa a Najeriya sayen kuri'ane da wayau. Shugaban kungiyar, Awwal Rafsanjani ne ya bayyana haka a wata hira da yayi da gidan talabijin na Channels, Awwal ya bayyana cewa tsarin sayen kuri'ane da wayau inda gwamnatin tarayya ke amfani da kudin baitilmani tana bayarwa. Yace dalilinsu na cewa haka shine cikin shekaru 3 da suka gabata karkashin mulkin APC bata kawo wannan tsari ba sai ana gab da yin zabe, ya kara da cewa koda kuwa ba salon sayen kuri'a bane da wayau dole Duniya zata kalleshi a haka.

Na Tabbata Da Umaru Musa Yar'adua Na Da Rai Da Jam'iyyar APC Zai Yi Saboda Adalcinta>>Hajia Bilkisu Kaikai

Image
Na Tabbata Da Umaru Musa Yar'adua Na Da Rai Da Jam'iyyar APC Zai Yi Saboda Adalcinta>>Hajia Bilkisu Kaikai Tsohuwar Mai ba tsohan Gwamna Ibrahim Shehu Shema shawara akan ilmin 'yaya mata, wadda ta dawo jamiyyar APC Hajiya Bilkisu Kaikai, ta bayyana cewa sakamakon irin ayyukan alherai da Kuma gina kasa da shugaban kasa Muhammadu Buhari, da Gwamna Masari ke Yi a jihar Katsina. Ta ce da Allah yasa Marigayi tsohan shugaban kasa malam Umaru Musa Yar'adua yana da rai da yanzu yana cikin jamiyyar APC. Hajiya Bilkisu Kaikai ta bayyana haka ne a Karamar Hukumar Kusada a wajen taron gangamin yakin neman zaben Gwamna Aminu Bello Masari da yake yi a shiyyar Daura. Bilkisu Kaikai ta cigaba da cewa duk wannan matsaloli na rashin tsaro da kasar nan ke fuskanta, Jamiyyar PDPce ta asassa shi da gangan. Yanzu Kuma shugaba Buhari da Gwamna Masari suna yin bakin kokarin su domin kawo karshen fitinu, don hakamu mu ma al'umma my cigaba da yin addua samun dawamamme zaman lafiya a ka...

Matsalar dake tsakanin Shugaba Buhari da Obasanjo

Image
Daga Shafin Abubakar A Adam babankyauta Babu yadda Za,ayi Azauna inuwa guda tsakanin Adalin Shugaban Najeriya Muhammadu buhari da Tsohon Shugaban Najeriya Cif Olusegun obasanjo Acikin Najeriya Domin Adalin Shugaban Najeriya Muhammadu buhari Shine Mutun Na farko dake yaki da Chin hanchi da Rashawa Acikin Najeriya A karkashin Mulkin Dimokaradiya janhoriya ta uku Acikin Najeriya baki daya Shi kuma tsohon Shugaban Najeriya Cif Olusegun Obasanjo Shine Mutun Na farko da yakawo Chin hanchi da Rashawa karkashin Mulkin Dimokaradiya jangoriya ta uku Acikin tarihin Najeriya Kamar yadda Muka Sani ne Lokacin da Obasanjo yazama Shugaban Najeriya 1999 karkashin Mulkin Dimokaradiya janhoriya ta uku baida Naira dubu dari tashi ta kan Shi domin Hatta kayan da Obasanjo yayi yakin Zabe dasu IBB ne ya siyammai su Amma yau Obasanjo Shine ya Mallaki biliyoyin daloli Acikin Najeriya Domin idan kuka kalli iya gidan gonan Obasanjo dake Otta kunsan Akwa dukiyar Alummar Najeriya Aciki Tsabar Daura Najeriya Akan t...

Buhari yayi kokari amma bazai iya ci gaba ba ya je gida ya huta>>PDP

Image
Buhari yayi kokari amma bazai iya ci gaba ba ya je gida ya huta>>PDP Jam'iyyar PDP ta bayyana cewa shugaban kasa, Muhammadu Buhari yayi kokari amma yanzu be da kuzarin ci gaba da mulki dan haka ya kamata ya je gida ya huta. Shugaban jam'iyyar Uche Secondus ne ya bayyana haka a wajan yakin neman zaben jam'iyyar, jiya a Kaduna, Secondus yace sake zaben Buhari kamar baiwa wasu boyayyun mutanene dama su ci gaba da juya kasarnan yanda suka ga dama domin ba Buharin ne ke mulki ba. Ya bukaci a zabi Atiku dan ya samar da ayyukan yi da kawar da yunwa. Shima Atikun da yake jawabi yace, APC ta yi Alkawarin habbaka tattalin arzikin kasarnan lokacin da ta karbi Mulki amma ba'a gani a kasa ba sannan ta yi Alkawarin samar da tsaro amma duk gashinan sai kashe-kashe ake samu.

Idan zaka kara aure gani ina jira>>Wata ta tallata kanta ga Atiku

Image
Idan zaka kara aure gani ina jira>>Wata ta tallata kanta ga Atiku Bayan da dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar PDP, Atiku Abubakar ya saka wasu hotunan yakin neman zabenshi da yayi a Kaduna inda yake nuna farun cikinshi, jama'a da dama masoyanshi sun bayyana farin cikinsu, ita kuwa wata ta tallata kantane ga Atikun. Matashiyar me suna, Cecilia ta bayyana wa Atikun cewa, lallai taro yayi taro, Ranka ya dade idan zaka kara aure, gani fa.

INEC ta ce Oby ta makara: Sai an yi zabe da ita

Image
INEC ta ce Oby ta makara: Sai an yi zabe da ita Hukumar zabe mai zaman kanta a Najeriya, INEC ta ce 'yar takarar shugabancin kasar a jam'iyyar ACPN Obiageli Ezekwesili ta makara wajen janye takararta a zaben 2019. Mai magana da yawun hukumar, Malam Aliyu Bello ya ce sashe na 35 na dokar zabe ta shekarar 2010, ya nuna cewa jam'iyya ko dan takara zai iya janye takararsa kwanaki 45 kafin ranar da za a kada kuri'a. Ya ce a zaben 2019, hukumar INEC ta ware 17 ga watan Nuwamba a matsayin rana ta karshe da 'yan takarar shugabancin kasa da na majalisar za su iya janyewa. Malam Aliyu ya ce tanadin dokar shi ne idan dan takara ya yi niyyar janyewa daga takararsa, sai ya ankarar da jam'iyyarsa ta hanyar rubuta wasika inda ita kuma jam'iyyar za ta sanar da hukumar zaben. Ya ce jam'iyyar ACPN ba ta sanar da hukumar INEC ba a kan lokaci, don haka hukumar za ta ci gaba da shirye-shiryenta na zabe yadda ya kamata. Oby Ezekwesili dai ta janye daga takarar shugabancin Naj...

Mazaje na rububin auren matar da mijinta ya sake ta saboda tace Buhari zata zaba

Image
Mazaje na rububin auren matar da mijinta ya sake ta saboda tace Buhari zata zaba Ga dukkan alamu matarnan da mijinta ya saketa dalilin dagewa da ta yi akan sai ta zabi shugaban kasa, Muhammadu Buhari a zabe me zuwa ba zata yi kwantai ba domin kuwa yanzu haka an samu mazaje sun yunkuro da cewa zasu aureta, duk da cewa dai wasu sun bayyana rashin kyautawar abinda ta wa mijin nata da shima hukuncin da ya dauka. Babban masoyin Shugaban Kasa a jihar Kano Auwal G Danbarno ya sha alwashin auren matar da mijinta ya sake saboda ta dage sai ta zabi Buhari.  Ya wallafa a shafinsa na facebook cewa, "Zan aureta ko ta kai shekaru ?ari, kuma ko kuturwa ce. Matar da mijinta ya sake ta kan za?en Buhari" Haka kuma shima wani da yake bayyana ra'ayinshi akan labarin da BBC suka wallafa ya bayyana cewa a shirye yake ya auri matar idan ta kammala Idda.

SIYASA BA DA GABA BA: Gwamna Tambuwal na Sakkawato ya karbi shugaba Buhari a filin jirgi

Image
SIYASA BA DA GABA BA: Gwamna Tambuwal na Sakkawato ya karbi shugaba Buhari a filin jirgi Gwamna Tambuwal ya karbi Shugaban Kasa, Muhammad Buhari a filin jirgin saman kasa da kasa na Sarkin Musulmi Abubakar Na Uku, a lokacin da ya isa jihar Sokoto domin yakin neman sake zaben shi karo na biyu a jihohin Sokoto da Kebbi, inda Shugaban kasa ya samu kyakkyawar tarbo ga dinbin mutanen da suka fito suna sai Baba, kafin ya wuce zuwa fadar mai Alfarma Sarkin Musulmi inda ya kai ziyara ta musammam.  Rariya

Zan Mayarwa Da Atiku Mota Da Kudaden Da Ya Ba Ni Domin Yi Masa Yakin Neman Zabe>>Rabi'u Biyora

Image
Zan Mayarwa Da Atiku Mota Da Kudaden Da Ya Ba Ni Domin Yi Masa Yakin Neman Zabe>>Rabi'u Biyora "Zai kasance babban kuskure gare ni na cigaba da amfani da motar da aka bani don na yi kamfen, tunda dai na bayyana cewa ba zan yi kamfen din ba. Hatta 'yan kudaden kashewar da aka bani duk suna nan a lissafe kuma zan mika su in sha Allah zuwa gobe. Ba zai yiwu in hana mutane hasashe akan wannan lamari ba, sai dai dole akwai cikakkiyar gaskiyar lamarin da ni Biyora na sani suma wadanda suka bani daga gidan dana koma a kwanakin baya suka sani. Na yanke shawarar dawowa tafiyata ta baya ne saboda wasu dalilan da nake ganin ta haka ne kawai zan fi samun saukin gudanar da rayuwata, koda kuwa naci gaba da yawo akan babur dina ne, tuni na saka an gyara mun shi don cigaba da zirga zirga akansa kamar yadda na saba a baya. Kalubale dole na sake fuskantarsa a yanzu kamar yadda na fuskanta a baya kila ma ya fi na baya yawa. In sha Allah bayanai za su fito ta yadda kowa zai fahimci dali...

Rabi'u Biyora Ya Dawo Tafiyar Buhari

Image
Rabi'u Biyora Ya Dawo Tafiyar Buhari Ga abinda ya rubuta ASSALAM ALAIKUM AL'UMMA... Sako Na Musammam  Da farko ina mika godiya mara iyaka a gareku tare da fatan Allah ya cigaba da yimana jagora a rayuwarmu gaba daya... Ina son amfanin da wannan dama na tunasar damu abun da muka sani tun tini dangane da yanayin siyasar wannan kasa (Nigeria), a tsakankaninmu yara, matsakaita da manyan mu ta yadda mafi akasari kan nemawa kansu bangaren siyasar da suke kyautata zaton zasu samu damar gudanar da ayyukansu da cikar burukansu ba tare da samun tsaiko ba.... Kusan sati uku kenan ana tattaunawa akan yanayin siyasar da Biyora ya samu kansa a cikinta, bayan da labari ya bayyana cewa na canza sheka zuwa tsagin gidan Alhaji Atiku Abubakar, bayan sanin da akayimun a bangaren tafiyar Baba Buhari, wannan abu ya janyo maganganu masu yawa musammam ga wadanda suke zaton kamar hakan bazai taba faruwa ba, wasu kuwa har gobe sun kasa aminta da cewa zan iya rabuwa da Baba Buhari a siyasance, duk da cew...

Ko a dajin Sambisa za'a ajiye akwatin zabe zamu je mu sakawa Buhari kuri'a>>Inji wani dan jihar Yobe

Image
Ko a dajin Sambisa za'a ajiye akwatin zabe zamu je mu sakawa Buhari kuri'a>>Inji wani dan jihar Yobe Wannan wani hoton masoyan shugaban kasa, Muhammadu Buharine a jihar Yobe inda yaje yakin neman zabe, jiya, hoton ya dauki hankula saboda irin sakonnin da mutanen ke dauke dashi a kan kwalayen da suke rike dasu. Daya daga cikin kwalayen yace, na yadda da Buhari fiye da yadda na yarda da kaina. Dayan kuwa yace, mu 'yan jihar Yobe dole mu sake zabenka a karo na biyu ko da kuwa a dajin Sambisa za'a ajiye akwatin zaben.